Kungiyar gwamnonin APC ta PGF ta musanta rahotannin da ke cewa an cire gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, daga shugabancin ƙungiyar.
A wata sanarwa da Darakta Janar na ƙungiyar, Folorusho Aluko, ya fitar ranar Laraba, PGF ta bayyana rahotannin a matsayin ƙarya da marasa tushe.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa ƙungiyar ta ce ba a gudanar da wani taro da aka yanke hukuncin cire Uzodimma daga mukaminsa ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa sakatariyar PGF ba ta da wani bayani ko matsaya da ta shafi cire shugaban ƙungiyar daga muƙaminsa.
Kungiyar ta ce har yanzu tana haɗe kai kuma tana ci gaba da gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.
PGF ta kuma buƙaci jama’a da magoya bayan APC da kafafen yaɗa labarai su yi watsi da rahotannin, tana mai jaddada cewa Gwamna Hope Uzodimma na ci gaba da samun goyon bayan gwamnonin APC.
