Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya sayi fom ɗin tsayawa takara da na nuna sha’awa domin neman kujerar Sanatan Bauchi ta Kudu a ƙarƙashin jam’iyyar Allied Peoples Movement (APM).
Gwamnan ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan dawowarsa daga Abuja, inda ya halarci taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) na jam’iyyar a ranar Alhamis.
A wani ci gaba na daban kuma, Sanatan da ke wakiltar mazabar Bauchi ta Tsakiya, Abdul Ahmed Ningi, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP
Ningi ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙar murabus da ya aike wa shugaban PDP na mazabar Ningi a karamar hukumar Ningi ta Jihar Bauchi.
Sanatan, wanda ya shafe sama da shekaru 20 yana cikin PDP, ya ce ya ɗauki wannan mataki ne sakamakon rikicin cikin gida da ya dade yana addabar jam’iyyar.
