DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Tuesday, July 7, 2026
HomeLabaraiBa zan mayar da Kwankwaso dan kallo ba idan na ci zabe...

Ba zan mayar da Kwankwaso dan kallo ba idan na ci zabe – Peter Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, zai kasance abokin tafiya a gwamnatinsa idan suka yi nasara a zaɓen 2027, ba kamar mataimakan shugaban ƙasa da ake warewa a matsayin ƴan kallo ba.

Obi ya bayyana hakan ne ranar Asabar bayan karɓar tikitin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, inda ya kuma sanar da Kwankwaso a matsayin abokin takararsa.

Kamar yadda Channels ya ruwaito, Obi ya ce gwamnatinsa za ta kasance mai haɗin kai da tuntuba, wadda mataimakin shugaban ƙasa ba zai zama “spare tyre” ba, sai dai cikakken abokin aiki wajen tafiyar da harkokin ƙasa.

Obi ya bayyana Kwankwaso a matsayin jagora mai muhimmanci wanda ke da irin manufofinsa musamman a fannonin ilimi da tsaro. Ya ce za su yi aiki tare domin magance matsalolin da suka addabi Nijeriya.

Ya kuma jaddada cewa tsaro zai kasance ɗaya daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa za ta bai wa fifiko, yana mai cewa babu wata ƙasa da za ta ci gaba idan al’ummarta na rayuwa cikin fargaba.

Ya ƙara da cewa burinsu shi ne gina Nijeriya mai haɗin kai da ƙarfafa cibiyoyin gwamnati domin samar da ci gaba mai ɗorewa.

Ukashatu Wakili
Ukashatu Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata