DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Friday, April 17, 2026
HomeLabaraiBudurwa ta haifi jaririn da gwajin DNA ya tabbatar da cewa na...

Budurwa ta haifi jaririn da gwajin DNA ya tabbatar da cewa na kakanta ne a jihar Neja

Wata budurwa mai shekara 16 ta haifi jariri namiji, inda aka ce kakanta mai suna Musa Gado ne mahaifin yaron.

Jaridar Punch ta rawaito cewa an tabbatar da wannan zargi ne bayan an gudanar da gwajin DNA wanda ya nuna kakanta ne suka yi mu’amalar aure har hakan ta faru.

Bayan da yarinyar ta samu juna biyu, ana zargin kakanta ya shawo kanta da ta zubar da cikin. Ta yi kokarin yin hakan ta hanyar shan wasu magunguna da allurai, amma hakan bai yi nasara ba.

Daga bisani, yarinyar mai juna biyu ta kai rahoto ofishin Hukumar Kare Hakkin Yara, inda aka ajiye ta a karkashin kulawa har zuwa lokacin da ta haifi jaririn namiji.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata