DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Tuesday, July 7, 2026
HomeSiyasaObi ba ya bukatar hadaka da PDP ko kawance da Atiku don...

Obi ba ya bukatar hadaka da PDP ko kawance da Atiku don kayar da Tinubu – NLC

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, baya bukatar haɗin kan jam’iyyar PDP ko wasu jiga-jigan siyasa irinsu Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da Nasiru El-rufa’I domin samun nasara a zaben 2027.

Wannan jawabi ya fito daga bakin Mataimakin shugaban kungiyar ta ƙasa, Farfesa Theophilus Ndubuaku, a wata hira ta musamman. Ya ce Peter Obi na da farin jini a tsakanin al’umma, kuma shi ne mutum mafi cancanta da zai iya gaba-da gaba a kokarin kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a babban zaben da ke tafe.

Farfesa Ndubuaku ya kuma ƙaryata jita-jitar da ke yawo kan cewa Peter Obi zai koma jam’iyyar PDP, yana mai cewa PDP ta zama jam’iyyar da ke cike da rikice-rikice da rudani a kan sahihancin manufarta.

Ya jaddada cewa Peter Obi da jam’iyyar Labour za su tsaya tsayin daka wajen gina sabon tsari mai inganci a siyasar Najeriya, ba tare da dogaro da tsofaffin tsari na raunanan jam’iyyu ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata