DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Tuesday, July 7, 2026
HomeKetareOusmane Sonko ya zama kakakin majalisar dokokin Senegal

Ousmane Sonko ya zama kakakin majalisar dokokin Senegal

Majalisar dokokin ƙasar Senegal ta zaɓi tsohon firaminista, Ousmane Sonko, a matsayin kakakin majalisar dokokin ƙasar bayan dawo da shi majalisar a zaman da ‘yan adawa suka kaurace wa halarta.
Jaridar Punch ta rawaito cewa Sonko, wanda shi kaɗai ne ya tsaya neman takarar, ya samu ƙuri’u 132 yayin da babu wani ɗan majalisa da ya kaɗa ƙuri’ar adawa da shi, sai mutum guda da ya kaurace wa jefa ƙuri’a.
Jami’in da ya jagoranci zaman majalisar, Ismael Diallo, ya bayyana cewa majalisar dokokin Senegal na da kujeru 165 gaba ɗaya.
Zaɓen Sonko na zuwa ne bayan sauye-sauyen siyasa da suka faru a ƙasar, inda ya rasa mukamin firaminista kafin daga baya aka dawo da shi cikin majalisar dokoki.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata