Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana damuwa da cewa dubban ‘yan gudun hijira a Nijeriya na iya komawa yankunan da ke cike da ragowar abubuwan fashewa, musamman yayin da ake rufe sansanoni ba tare da samar musu da wurin zama a madadin muhallansu ba.
Masana a taron kasa da kasa da aka gudanar a hedikwatar MDD a Geneva sun ce raguwar tallafi a kasashe kamar Nijeriya da Afghanistan na kara jefa fararen hula cikin hadarin bamabaman da ba su tashi ba kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Shugaban shirin kawar da abubuwa masu fashewa na MDD a Nijeriya, Mista Edwin Faigmane, ya ce UNMAS ta horas da sojoji, ‘yan sanda da jami’an tsaron farar hula kan yadda ake kare kai da kuma yadda ake gano abubuwan fashewa a wuraren da ake fama da rashin tsaro.
Faigmane ya bayyana cewa horon ya fara haifar da sakamako, domin ana samun rahotanni daga al’ummomi da jami’an tsaro game da gano abubuwan fashewa da kuma mika su ga hukumomi da rundunonin tsaro.



