DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan gudun hijira da ke komawa muhallansu a Nijeriya na iya fuskantar barazanar ababen fashewa a yankunansu – MDD

-

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana damuwa da cewa dubban ‘yan gudun hijira a Nijeriya na iya komawa yankunan da ke cike da ragowar abubuwan fashewa, musamman yayin da ake rufe sansanoni ba tare da samar musu da wurin zama a madadin muhallansu ba.

Masana a taron kasa da kasa da aka gudanar a hedikwatar MDD a Geneva sun ce raguwar tallafi a kasashe kamar Nijeriya da Afghanistan na kara jefa fararen hula cikin hadarin bamabaman da ba su tashi ba kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Shugaban shirin kawar da abubuwa masu fashewa na MDD a Nijeriya, Mista Edwin Faigmane, ya ce UNMAS ta horas da sojoji, ‘yan sanda da jami’an tsaron farar hula kan yadda ake kare kai da kuma yadda ake gano abubuwan fashewa a wuraren da ake fama da rashin tsaro.

Faigmane ya bayyana cewa horon ya fara haifar da sakamako, domin ana samun rahotanni daga al’ummomi da jami’an tsaro game da gano abubuwan fashewa da kuma mika su ga hukumomi da rundunonin tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara