Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKwankwaso ya bayyana masu digirin digirgir “Phd” 300 da Gidauniyar Kwankwasiyya ta...

Kwankwaso ya bayyana masu digirin digirgir “Phd” 300 da Gidauniyar Kwankwasiyya ta samar a taronta na shekara-shekara

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya bayyana sama da masu digiri na uku (PhD) 300 da aka samar ta hanyar shirin tallafin karatu na Kwankwasiyya a taron farko na shekara-shekara na masu cin gajiyar tallafin a Kano.

Kwankwaso ya bayyana ilimi a matsayin gadon da shugaba zai iya bari ga al’umma, yana mai cewa saka jari mai dorewa a fannin shi ne ainihin ma’aunin kyakkyawan shugabanci.

A jawabin da ya yi a taron a ranar Laraba, Kwankwaso ya ce wannan taro tarihi ne ga Jihar Kano da Nijeriya baki ɗaya, inda ya lura cewa taron ya ba da darussa kan shugabanci, dorewa, da hangen nesa, tare da jaddada cewa auna shugabanci ya kamata ya dogara ne kan tasirinsa mai dorewa ga rayuwar ‘yan ƙasa.

Kwankwaso ya kuma bayyana cewa bayan zaɓen 2019, lokacin da gwamnati ta dakatar da tallafin ɗalibai a ƙasashen waje, ya ɗauki nauyin ci-gaba da shirin ta hannun Gidauniyar Ci-gaban Kwankwasiyya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata