DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama magidancin da ake zargin ya yi ajalin matarsa da fartanya a jihar Kebbi

-

Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta kama wani mutum mai shekara 30, Suleman Mamuda, bisa zargin halaka matarsa Umaima Maidawa a unguwar Bayawa da ke Karamar Hukumar Augie ta jihar.

Mai magana da yawun rundunar, SP Bashir Usman, ya ce ana zargin Mamuda da dukan matarsa da sandar iccen fartanya, lamarin da ya yi sanadin ajalinta.

Google search engine

Ya bayyana cewa bayan faruwar lamarin, wanda ake zargin ya tsere daga yankin, amma daga bisani jami’an tsaro suka gano inda yake tare da cafke shi sakamakon bincike da bayanan sirri daga al’ummar yankin.

Rundunar ta ce Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Umar Mohammed Hadejia, ya bayar da umarnin mika shi zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike da gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara