Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuSarkin Musulmi ya ayyana Talata 20 ga Janairu a matsayin 1 ga...

Sarkin Musulmi ya ayyana Talata 20 ga Janairu a matsayin 1 ga watan Sha’aban 1447AH

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Nijeriya (NSCIA), ya ayyana Talata 20 ga watan Janairu, 2026, a matsayin rana ta farko ta watan Sha’aban, 1447 bayan Hijira.

 

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa ga manema labarai da aka fitar a ranar 19 ga Janairu, 2026, daga fadar Sarkin Musulmi da ke Sokoto.

 

Sanarwar, wadda Farfesa Sambo Wali Junaidu, Waziri na Sokoto kuma Shugaban Kwamitin Ba da Shawara kan Harkokin Addini na Majalisar Sarkin Musulmi ya rattaba hannu a kai, ta ce an yanke wannan hukunci ne bayan cikakken bincike da rahotannin ganin jinjirin watan da aka tattara daga sassa daban-daban na ƙasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata