DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, July 8, 2026
HomeLabaraiShugaban majalisar dokokin jihar Borno ya soki rashin sanya hoton Kashim Shettima...

Shugaban majalisar dokokin jihar Borno ya soki rashin sanya hoton Kashim Shettima a taron jam’iyyar APC

Shugaban majalisar dokokin jihar Borno, Abdulkarim Lawan, ya nuna rashin jin daɗinsa kan rashin sanya hoton mataimakin shugaban Nijeriya, Sanata Kashim Shettima a hotunan da aka yi amfani da su wajen wani taron jam’iyyar APC da ake gudanarwa a Maiduguri, babban birnin jihar.

Abdulkarim Lawan ya bayyana hakan ne a yayin taron, inda ya ce abin bai dace ba a ki saka hoton mataimakin shugaban kasa ba, musamman ganin cewa taron na gudana ne a mahaifarsa, kuma shi ne wakilin Arewa maso Gabas a matsayin mataimakin shugaban ƙasa.

Ya ƙara da cewa irin wannan rashin sanya hoton Shettima ne ya jawo rikici a taron APC na Gombe a bara, yana mai gargadin cewa ya kamata a kauce wa maimaita kuskuren.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata