DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bisa radin kaina na yi murabus daga shugabancin hukumar NAHCON – Farfesa Abdullahi Pakistan

-

Shugaban Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Nijeriya (NAHCON), Farfesa Sheikh Abdullahi Saleh Usman, ya sanar da yin murabus daga mukaminsa na Shugaba kuma Babban Darakta na hukumar, daga ranar Litinin, 9 ga Fabrairu, 2026.

A cikin wata sanarwar da ya aike wa manema labarai, Farfesa Usman ya ce murabus din nasa ya samo asali ne daga dalilai na kansa kawai, bayan yin addu’a da tuntubar iyalansa, ba tare da wata matsala ko sabani da gwamnati ko hukumar ba.

Google search engine

Ya ce ya mika rubutacciyar wasikar murabus dinsa ga Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa tanadin Sashe na 3(6) na Dokar Kafa Hukumar NAHCON ta 2006.

Tsohon shugaban hukumar ya nuna godiya ga Shugaban Kasa Bola Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima bisa amincewa da goyon bayan da suka ba shi a lokacin da yake rike da mukamin, tare da yaba wa mambobin kwamitin gudanarwa, ma’aikatan NAHCON da sauran abokan hulda ciki har da hukumomin aikin hajji na jihohi da mahukuntan Saudiyya.

Yana mai addu’a ga maniyyatan Nijeriya da Hajji Mabrur.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara