DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Tuesday, July 7, 2026
HomeLabaraiMuna neman dauki kan yawan harin da dorinar ruwa ke kawo mana...

Muna neman dauki kan yawan harin da dorinar ruwa ke kawo mana – Dan majalisar tarayya a Gombe

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Yamaltu/Deba a Jihar Gombe, Inuwa Garba, ya roki gwamnatin tarayya su kawo musu dauki kan hare-haren dorinar ruwa da suka addabi mazauna yankinsa.

Garba ya gabatar da wannan bukata ne a zaman da mataimakin kakakin majalisar wakilai Benjamin Kalu ya jagoranta, inda ya bayyana cewa hare-haren sun yi sanadin rasa rayukan wasu mafarauta da manoma a bakin koguna da gonaki.

Ya kara da cewa, hare-haren da ke faruwa a yankin sun haifar da tsoro da tashin hankali, abin da ya tilasta wasu manoma da masu kamun kifi barin aikinsu, lamarin kuma na kara ta’azzara talauci da rashin abinci.

A ranar 5 ga watan Oktoba, wata dorinar ruwa ta afkawa masunta a cikin kwale-kwale, inda ta kashe mutum daya mai suna Yahaya Bawa, ta kuma jikkata wasu da dama kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata