DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kashim Shettima ya tafi Brazil domin halartar taron sauyin yanayi karo na 30

-

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bar Abuja zuwa Brazil domin wakiltar shugaba Bola Tinubu a babban taron sauyin yanayi na Majalisar Dinkin Duniya karo na 30 da za a gudanar a birnin Belém na kasar Brazil.

Taron, wanda shugaban Brazil, Luiz Inácio Lula da Silva ke jagoranta tare da hadin guiwar wasu kasashe, zai gudana daga ranar 6 zuwa 7 ga watan Nuwamba, inda za a tattauna batutuwan da suka shafi kariyar dazuka, halittu, da adalcin yanayi.

Google search engine

Mai magana da yawun ofishin mataimakin shugaban kasa, Stanley Nkwocha, ya bayyana cewa Shettima zai gabatar da jawabin Nijeriya kan sauyin yanayi, sannan ya halarci tarukan kwamitoci da za su tattauna batun canjin makamashi da yarjejeniyar Paris.

Haka kuma, Shettima zai yi ganawa da shugabanni da masu ruwa da tsaki don tattauna yadda Nijeriya za ta shiga kasuwar carbon finance da ake sa ran za ta samar da har dala biliyan uku a duk shekara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara