DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya rantsar da Doro da Udeh a matsayin ministoci

-

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis, ya rantsar da Dr. Bernard Doro da Dr. Kingsley Udeh a matsayin sababbin ministoci, kafin fara zaman majalisar zartarwa na farko tun watan Yuli.

Dr. Doro, kwararren likita daga Filato, ya maye gurbin Farfesa Nentawe Yilwatda, yayin da Dr. Udeh daga Enugu ya maye gurbin Uche Nnaji wanda ya yi murabus kan takardun karatu.

Google search engine

Bayan rantsuwar, Tinubu ya jagoranci zaman majalisar inda ministan kudi, Wale Edun, ya bayyana cewa dawowar Nijeriya kasuwar lamuni ta duniya ta jawo karuwar sha’awar masu saka jari, inda kudin Eurobond ya samu karin bukata mai yawa.

Edun ya ce gwamnati za ta cigaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki, ta inganta kasuwanci, da tabbatar da rarraba ribar ci-gaba ga ’yan kasa kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara