Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiSanata Barau ya yi martani ga gwamnatin Kano bayan ta zarge shi...

Sanata Barau ya yi martani ga gwamnatin Kano bayan ta zarge shi da Ganduje da yunkurin kawo cikas ga tsaro

Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Barau I. Jibrin, ya shawarci gwamnatin Kano ta daina sanya siyasa a cikin batun tsaron jihar.

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana cewa wasu kalamai da tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje da Sanata Barau suka yi a kwanan nan, suna da hatsarin iya kawo cikas ga kokarin tabbatar da tsaro da gwamnatin jiha da ta tarayya ke yi a yanzu.

Sai dai a cikin sanarwar da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Ismail Mudashir, ya fitar, Sanata Barau ya bayyana zargin gwamnatin jihar a matsayin maras tushe, yana mai kalubalantar gwamnatin ta fitar da bidiyon da ke nuna ya yi maganar da za ta iya ta’azzara matsalar tsaro.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata