DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, April 22, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Bauchi ta umurci masu son takara da ke rike da mukamai...

Gwamnatin Bauchi ta umurci masu son takara da ke rike da mukamai da su ajiye mukamansu

Gwamnatin jihar Bauchi ta umurci dukkan masu rike da mukaman siyasa da ke da niyyar tsayawa takara a zabukan fidda gwani da ke tafe da su yi murabus kafin ranar Juma’a, 24 ga Afrilu, 2026.

A wata sanarwa da mai ba gwamnan jihar shawara kan harkokin yada labarai, Mukhtar Gidado ya fitar, ta ce wannan mataki ya dace da dokar zabe ta 2026, domin tabbatar da bin doka da oda a harkokin zabe.

Sanarwar ta kara da cewa gwamnatin ta yaba wa irin gudunmawar da wadannan mutane suka bayar wajen ci gaban jihar, tare da yi musu fatan alheri a kokarinsu na na shiga zaɓe

Haka kuma, an umarce su da su mika dukkan kadarorin gwamnati da ke hannunsu tare da ayyukansu ga wadanda suka dace a ma’aikatunsu kafin barin aikin nasu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata