DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, July 8, 2026
HomeBabban Labari Na yi mamakin yadda Majalisar dattawa ta ayyana nemana ruwa a jallo...

Na yi mamakin yadda Majalisar dattawa ta ayyana nemana ruwa a jallo – Mele Kyari

Tsohon Babban Daraktan kamfanin man fetur a Nijeriya NNPCL, Mele Kyari, ya bayyana matakin da Majalisar dattawa ta dauka na fitar sanarwar nemanshi ruwa a jallo a matsayin abin mamaki matuka, yana mai cewa tun tuni ya sanar da kwamitin cewa yana jinya a wata kasa da ke wajen Nijeriya.

Kyari ya bayyana hakan ne a wata wasika da ya aikewa shugaban kwamitin majalisar dattawa bayan majalisar ta ba da umarnin kama shi sakamakon rashin halartar zaman binciken da ake yi kan wasu harkokin kudaden NNPCL.

A cewarsa, tun ranar 11 ga Mayu, 2026 ya rubuta wa kwamitin yana sanar da su cewa yana karbar magani a wata kasa da ke wajen Nijeriya, tare da bayyana shirinsa na amsa gayyatar da zarar ya dawo gida.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata