Gwamnan jihar Jigawa, Malam Umar A. Namadi, ya amince da naɗin Dakta Lawan Ahmed Muhammad Sani a matsayin sabon sarkin masarautar Gumel na 17, domin maye gurbin mahaifinsa da ya rasu kwanan nan.
Sakataren gwamnatin jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a madadin gwamnatin jihar a ranar Lahadi, inda ya bayyana cewa amincewar ta biyo bayan shawarar da majalisar masu zaɓen sarki ta masarautar Gumel da kuma majalisar sarakunan jihar Jigawa suka miƙa wa gwamnan.
Sabon sarkin na 17 zai gaji mahaifinsa, marigayi Alhaji Dakta Ahmed Muhammad Sani II, wanda ya riga mu gidan gaskiya a ranar Alhamis, 3 ga watan Satumban 2026, bayan kwashe shekaru 46 yana mulkin masarautar ta Gumel.
Kafin naɗin nasa a matsayin sabon sarkin Gumel, Dakta Lawan Ahmed Muhammad Sani yana riƙe da sarautar Chiroman Gumel, kuma shi ne daraktan tsaron intanet a Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA).
Gwamna Namadi ya nuna godiyarsa ga majalisar masu zaɓen sarkin Gumel a ƙarƙashin jagorancin Wazirin Gumel, Alhaji Adamu Muhammad Nasoro, da kuma sarakunan Hadejia, Kazaure, Ringim, da Dutse da ke cikin majalisar sarakunan jihar kan shawarwarin da suka bayar wajen zaɓen sabon sarkin.
A madadin gwamnatin jihar Jigawa, gwamnan ya taya sabon sarkin murna tare da yi masa fatan samun nasarar gudanar da shugabanci mai albarka ga masarautar Gumel da ƙasa baki ɗaya.
