Jam’iyyar APC ta mayar da martani kan zargin da tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi cewa an ware kudin Service-Wide Vote na kasafin kudin shekarar 2026 domin daukar nauyin yakin neman sake zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu a 2027.
A cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar APC na kasa, Felix Morka, ya sanya wa hannu a Abuja ranar 22 ga Yuli, 2026, jam’iyyar ta bayyana zargin Atiku a matsayin wanda ba shi da hujja, tana mai cewa ya samo shi ne daga zato kawai da nufin yaudarar al’umma da kuma dauke hankalin ‘yan Nijeriya daga nasarorin da gwamnatin Tinubu ke ikirarin samu.
APC ta ce abin da ake kira Service-Wide Vote wata hanya ce ta kasafin kudi da aka dade ana amfani da ita wajen biyan wasu bukatun gwamnati baki daya da kuma kudaden da ba a yi hasashensu ba, wadanda za su iya tasowa bayan amincewa da kasafin kudin shekara.
Jam’iyyar ta ce Service-Wide Vote ba wani asusun boye ko haramtaccen asusun gwamnati ba ne, kamar yadda ta ce Atiku ya yi ikirari ba tare da gabatar da wata hujja ba.
APC ta kuma zargi Atiku da yin amfani da kalaman da ba su da tushe wajen sukar gwamnatin Tinubu, tana mai cewa tsohon mataimakin shugaban kasar bai gabatar da wata hujja da za ta tabbatar da zargin da ya yi ba.
Jam’iyyar ta bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen aiwatar da shirye-shiryen da take ganin za su farfado da tattalin arzikin kasa da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.
Daga cikin shirye-shiryen da APC ta ambata akwai asusun ba da lamunin karatu na Nijeriya (NELFUND), wanda ta ce ya taimaka wa kusan dalibai miliyan biyu wajen samun damar karatun gaba da sakandare, da aiwatar da sabon mafi karancin albashi na kasa.
Sauran shirye-shiryen sun hada da tsarin bayar da lamunin sayayya ga ‘yan kasa, shirin amfani da iskar gas din CNG domin rage tsadar sufuri, tallafin abinci ga iyalai masu karamin karfi, da kara zuba jari a bangarorin more rayuwa, kiwon lafiya da noma.
APC ta ce gwamnatin Tinubu na kuma aiwatar da sauye-sauyen haraji da nufin saukaka tsarin haraji, bunkasa tattalin arziki da rage nauyin haraji ga masu karamin karfi.
Jam’iyyar ta jaddada cewa ita da gwamnatin tarayya za su ci gaba da mayar da hankali kan aiwatar da manufofin gwamnatin Tinubu ta Renewed Hope, da za ta sake gina tattalin arzikin kasa, karfafa sauye-sauyen hukumomi da fadada ayyukan more rayuwa domin inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.
