Jam’iyyar ADC ta ce dimokuraɗiyya ta gaza kawo sauyi mai ma’ana a rayuwar talakawan Nijeriya a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
A wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, ADC ta ce auna nasarar dimokuraɗiyya bai kamata ya ta’allaka ga yawan shekarun mulkin farar hula kaɗai ba.
Jam’iyyar ta ce a maimakon haka, ya kamata a duba tasirin dimokuraɗiyya a rayuwar jama’a da walwalarsu ta yau da kullum.
