DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Tuesday, July 7, 2026
HomeLabaraiGwamnatin jihar Kebbi ta rufe dukkanin makarantun gwamnati da masu zaman kansu...

Gwamnatin jihar Kebbi ta rufe dukkanin makarantun gwamnati da masu zaman kansu saboda barazanar tsaro a jihar

Gwamnatin jihar Kebbi ta rufe dukkan makarantun sakandare na gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihar saboda karuwar barazanar tsaro.

Hakan ya shafi manyan makarantu na jihar, ban da kwalejin koyon jinya ta Birnin Kebbi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A cikin sanarwar da kwamishinonin ilimi Halima Bande da Isa Abubakar-Tunga suka fitar, gwamnati ta ce matakin kariya ne bayan hare-hare da garkuwa da ’yan mata a Maga inda suka ce dole ne a tabbatar da lafiyar dalibai da ma’aikata a yanzu.

Matakin ya shafi daruruwan makarantu a kananan hukumomi 21, yayin da iyaye da dama ke cikin fargaba saboda hare-haren da suka auku kwanakin baya.

Abubakar-Tunga ya ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar tsaro kuma za a sanar da sabon ranar dawowa idan yanayi ya inganta.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata