Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Nijeriya, Femi Gbajabiamila, ya buƙaci ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, da ya ci gaba da zama a jam’iyyar adawa ta ADC tare da ƙarfafa gwagwarmayarsa a cikinta.
Gbajabiamila ya bayyana hakan ne yayin da yake yaba wa irin rawar da Abejide ke takawa a siyasar majalisa, yana mai cewa abin da yake yi yana da tasiri.
Ya ce ya kamata Abejide ya tsaya tsayin daka, ya ci gaba da fafutuka tare da ƙarfafa matsayinsa a cikin jam’iyyar.
A cewarsa, irin wannan jajircewa na taimakawa wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da samar da sahihin wakilci a majalisa.
Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sauya sheƙa tsakanin ‘yan majalisa gabanin zaɓen 2027.
