Gwamnatin Nijeriya ta ce bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta bana zai zama wata dama ta nuna nasarorin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu da kuma ci gaban da aka samu wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da bunƙasa ƙasa.
Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ne ya bayyana hakan ranar Talata a Abuja yayin ƙaddamar da Kwamitin Tsare-tsare na Ma’aikatu (IMC) domin shirya bikin Ranar Dimokuraɗiyya karo na 27.
Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, Akume ya ce bikin ranar 12 ga Yuni zai bai wa gwamnati damar bayyana wa ‘yan Nijeriya irin ci gaban da aka samu wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya, aiwatar da sauye-sauye da kuma sake fasalin ƙasa duk da ƙalubalen tattalin arziki da ake fuskanta.
Akume ya bayyana ranar Dimokuraɗiyya a matsayin lokaci na tunawa da tafiyar dimokuraɗiyyar Nijeriya da kuma sabunta alƙawarin gwamnati na kare ƙa’idojin dimokuraɗiyya da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.
Ya kuma karrama jaruman gwagwarmayar ranar 12 ga Yunin 1993 musamman marigayi Cif Moshood Kashimawo Olawale (MKO) Abiola, yana mai cewa sadaukarwarsu ce ta taimaka wajen tabbatar da ranar 12 ga Yuni a matsayin Ranar Dimokuraɗiyyar Nijeriya.
