Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, John Odigie Oyegun, ya bayyana cewa jam’iyyar ADC ta shirya karɓe mulki daga hannun Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027.
Oyegun ya bayyana hakan ne yayin babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, inda ya ce jam’iyyar ADC ta shirya tsaf domin shimfiɗa sabon salon mulki a Nijeriya.
A cewarsa, duk da arziƙin da Nijeriya ke da shi, har yanzu al’umma na fama da matsin tattalin arziki, abin da ya danganta da gazawar shugabanci a tsawon shekar
