DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, May 13, 2026
HomeSiyasaAn rantsar da Murtala Sule Garo a matsayin mataimakin Gwamnan Kano

An rantsar da Murtala Sule Garo a matsayin mataimakin Gwamnan Kano

An rantsar da Murtala Sule Garo a matsayin mataimakin Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano.

Wakilin DCL Hausa, Sadiq Muhammad Fagge, ya ruwaito cewa Murtala Garo, tsohon dan takarar mataimakin gwamnan Kano a zaben 2023, ya sha rantsuwar ne yayin wani taro da ya gudana a fadar gwamnati a yau Talata.

Wannan ya kawo karshen shafe makonni cikin rashin tabbas kan wanda zai maye gurbin Comrade Aminu Abdulsalam Gwarzo, wanda yayi murabus bayan sakamakon raba hanya a siyasa.

Kafin wannan lokaci dai, Gwamna Abba ya aike da sunan Murtala da Gwamna Abba ga majalisar dokokin Kano domin tantance shi a matsayin mataimakinsa.

Kamar yadda rahotanni da kuma majiyoyi suka nuna, an zabo Murtala Sule Garo ne, biyo bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC.

A yayin rantsuwar, an hangi fuskokin wasu jiga-jigai a cikin jam’iyyar APC irin su Abdullahi Umar Ganduje, Malam Ibrahim Shekarau, Sanata Barau Jibrin da sauran manyan ‘yan siyasa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata