Dan majalisar dokokin Jihar Borno mai wakiltar mazabar Magumeri, Honarabul Audu Mustapha Ganga, ya fashe da kuka yayin da yake roƙon al’ummarsa su mara masa baya domin sake tsayawa takara karo na biyar.
Rahotanni sun ce ɗan majalisar, wanda ya shafe shekara 16 yana wakiltar mazabar, ya yi roƙon ne bayan wasu masu ruwa da tsaki sun fara neman sabon wakilci a yankin.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, Ganga ya ce duk da cewa ya fito daga gidan talakawa, ya yi ayyuka da dama ga al’ummarsa.
Ya ce, “Kun san na fito daga gida mai talauci, amma na yi muku abubuwa da dama. Ina alƙawarin ba ku kyakkyawan wakilci idan aka sake ba ni dama.”
Rahotanni sun kuma nuna cewa mutane shida sun riga sun sayi fom ɗin neman takarar kujerarsa.
