DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, May 13, 2026
HomeLabaraiDan majalisar Borno ya fashe da kuka yana neman goyon bayan wa’adi...

Dan majalisar Borno ya fashe da kuka yana neman goyon bayan wa’adi na biyar

Dan majalisar dokokin Jihar Borno mai wakiltar mazabar Magumeri, Honarabul Audu Mustapha Ganga, ya fashe da kuka yayin da yake roƙon al’ummarsa su mara masa baya domin sake tsayawa takara karo na biyar.

Rahotanni sun ce ɗan majalisar, wanda ya shafe shekara 16 yana wakiltar mazabar, ya yi roƙon ne bayan wasu masu ruwa da tsaki sun fara neman sabon wakilci a yankin.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, Ganga ya ce duk da cewa ya fito daga gidan talakawa, ya yi ayyuka da dama ga al’ummarsa.

Ya ce, “Kun san na fito daga gida mai talauci, amma na yi muku abubuwa da dama. Ina alƙawarin ba ku kyakkyawan wakilci idan aka sake ba ni dama.”

Rahotanni sun kuma nuna cewa mutane shida sun riga sun sayi fom ɗin neman takarar kujerarsa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata