DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, July 8, 2026
HomeSiyasaMajalisar da ba za ta iya cewa shugaban kasa a'a ba, ba...

Majalisar da ba za ta iya cewa shugaban kasa a’a ba, ba majalisa ba ce – Bukola Saraki

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dokta Bukola Saraki, ya ce ’yancin cin gashin kan majalisa na da matuƙar muhimmanci ga dorewar dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Saraki ya bayyana haka ne yayin wani taron lacca na ranar 12 ga Yuni da ƙungiyar Covenant Nation ta shirya, inda ya jaddada cewa ya kamata majalisa ta riƙa tantance duk wasu shawarwari daga ɓangaren zartarwa kafin amincewa da su.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa Saraki ya ce majalisar da ke karɓar dukkan buƙatun gwamnati tare da amincewa da su ba tare da bincike da tantancewa ba, ba ta cika nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mata ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata