DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, May 13, 2026
HomeSiyasaSanata Danjuma Goje yaƙi karbar sasancin kan takararsa ta Sanatan Gombe a...

Sanata Danjuma Goje yaƙi karbar sasancin kan takararsa ta Sanatan Gombe a APC

Sanatan da ke wakiltar yankin Gombe ta Tsakiya, Muhammad Danjuma Goje, ya yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta hanyar “consensus” da jam’iyyar APC a jihar Gombe ta ɗauka.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa shugabannin jam’iyyar sun amince da DCP Mohammed Ahmadu Deba (mai ritaya) a matsayin ɗan takarar APC na kujera da Goje ke riƙe da ita, a wani taro da aka gudanar ranar Lahadi ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

Sai dai a wata sanarwa da hadiminsa kan harkokin shari’a, Barrista Saidu Mu’azu Kumo, ya fitar, Sanata Goje — wanda ke neman wa’adi na biyar a Majalisar Dattawa — ya ce taron “consensus” ɗin bai haɗa da dukkan ‘yan takarar da aka tantance ba, domin ya shafi Gwamna Yahaya ne kawai tare da wasu kaɗan daga cikin masu neman takarar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata