Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, na jam’iyyar Accord, ya sake lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar a ranar Asabar.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa hukumar zaɓen Nijeriya (INEC) ta bayyana Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan kammala tattara sakamakon daga ƙananan hukumomi 30 na jihar.
Adeleke ya samu ƙuri’u 511,067, inda ya doke babban abokin hamayyarsa, Bola Oyebamiji na jam’iyyar APC, wanda ya samu ƙuri’u 444,815.
Dan takarar jam’iyyar ADC ya zo na uku da ƙuri’u 17,180.
Wannan sakamakon ya nuna cewa Adeleke ya samu tazarar ƙuri’u 66,252 tsakaninsa da ɗan takarar APC.
Jami’in da ya bayyana sakamakon, Farfesa Joshua Ogunwole, wanda shi ne Mataimakin Shugaban Gwamnatin tarayya ta Ekiti, ya sanar da sakamakon a madadin INEC.
A cewar alkaluman ƙarshe, ya nuna cewa an yi wa mutum 2,339,544 masu zaɓe rajista, yayin da 1,010,684 aka tantance mutum domin kaɗa ƙuri’a.
An samu jimillar ƙuri’u 1,005,800 da aka kaɗa, daga cikinsu 985,079 ne ingantattu, yayin da aka ƙi amincewa da 20,721.
Nasarar ta bai wa Adeleke damar ci gaba da zama gwamnan Osun na wani wa’adi na biyu, bayan ya sake doke ɗan takarar APC a zaɓen da aka yi da zazzafar hamayya.
