Mai horas da tawagar kasar Brazil, kuma tsohon kocin Real Madrid Carlo Ancelotti ya bayyana cewa kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain na da babbar damar lashe kofin zakarun nahiyar Turai ‘UEFA Champions League’ a wannan kakar, wanda zai zama na biyu a tarihinsu idan hakan ta tabbata.
Wannan hasashe na Ancelotti ya jawo muhawara, musamman ganin yadda PSG ke ƙoƙarin kafa cikakkiyar ƙungiya mai ƙarfi da tasiri a nahiyar Turai tsawon shekaru, kamar yadda Fabrizio Romano ya wallafa.
Idan PSG ta cimma wannan buri, zai zama babban tarihi ga ƙungiyar, tare da ƙara tabbatar da matsayinta a cikin manyan kulob ɗin Turai.
Sai dai kuma masana da magoya bayan kwallon kafa na nuni da cewa akwai babban kalubale a gabanta kafin cimma wannan nasara, kasancewar akwai ƙungiyoyi masu ƙarfi da ke fafatawa a gasar.
