DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai fargabar yajin aikin NLC ba zai yi tasirin da ake bukata ba

-

Google search engine

Bankuna da hukumomin gwamnati da ke biyayya ga kungiyar
kwadago ta NLC a Najeriya sun kauracewa guraren ayyukan su, yayin da yajin aikin
ya doshi sa’o’I 24.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya NLC ya ruwaito
cewa baki daya bankuna basu yi aiki a fadin kasar ba, yayin da wasu daga cikin
ma’aikatun gwamnati suka fita aiki wasu kuma suka zauna a gida.

Tun farko dai kungiyar NLC ce ta kuduri aniyar tafiya yajin
aikin na kwanaki biyu don nunawa gwamnatin kasar bacin ranta a game da rashin
mayar da tallafin man fetur da ya haddasa tsadar rayuwa.

A cikin sanarwar da kungiyar ta fitar ta ce zata kuma tsunduma
wani yajin aikin na sai baba ta gani nan da makonni biyu masu zuwa matukar
gwamnati bata dauki matakin gyara bayan wannan yajin aikin da suka aiwatar ba.

DCL Hausa ta gano yadda mambobin na kungiyar NLC suka kulle
kofofin shiga gidan talabijin din NTA na kasa da na Radio don hana ma’aikata shiga.

To amma dai masana a kasar na ganin zai yi wuya
wannan yajin aikin yayi tasiri la’akari da barakar da ke tsakanin kungiyoyin
kwadago guda biyu na NLC da TUC, kasancewar TUC ta barranta kanta da mambobin
ta daga wannan yajin aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara