‘Yan majalisar dokokin jihar Rivers sun fara tantance sunayen mutanen da gwamnan jihar Siminalayi Fubara ya gabatar domin nada su a matsayin kwamishinoni.
Rahotanni sun nuna cewa mutum tara ne aka raka zuwa majalisar da misalin karfe 10 na safe a ranar Litinin domin fara tantance su.
Mutanen da aka gabatar sun hada da Datonye Alasia, Tonye Bellgam, Temple Nwofor, Peters Nwagor, Charity Deemua, Tamuno Williams, Lekue Kenneth, Otonye TKD Amachree, da kuma Amairigha Hart.
A cikin wani bidiyo da tashar Arise TV ta watsa, an ga kowane daga cikin wadanda aka gabatar yana hawa mumbari yana gabatar da kansa tare da amsa tambayoyin ‘yan majalisar.
