Saturday, March 21, 2026
HomeLabaraiPeter Obi ya soki shugabannin Nijeriya kan rashin mayar da hankali kan...

Peter Obi ya soki shugabannin Nijeriya kan rashin mayar da hankali kan matsalar tsaro

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi, ya soki shugabannin Nijeriya saboda, sun fi mayar da hankali kan zaɓen da ke tafe maimakon magance matsalar tsaro da ke ƙara tsananta a ƙasar.

A wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na sada zumunta, Obi ya ce ƙasar na cikin mawuyacin hali na tsaro, inda hare-haren ‘yan ta’adda da sace sacen mutane ke ƙaruwa a sassa daban-daban.

Google search engine

Ya kawo misali da hare-haren baya bayannan da aka kai jihar Borno da ya yi sanadiyyar mutane da dama tare da sace mata kusan 100.

Obi ya kuma nuna damuwa kan rahotannin matsalar tsaro a jihohin Nasarawa, Kogi da Benue inda mazauna yankuna ke cewa ‘yan ta’adda suna mamaye gonaki da dazuka, lamarin da ke tilasta wa mutane barin gidajensu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata