Gwamnatin Iran ta bayyana cewa ba ta da niyyar fara tattaunawa da Amurka a halin yanzu, yayin da rikicin da ya barke tsakanin kasashen aka shiga rana ta 11, tare da ci gaba da kai hare-haren makamai masu linzami a yankin Gabas ta Tsakiya.
Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana haka a wata hira da tashar PBS News, inda ya ce Iran ba ta ganin tattaunawa da Amurka a matsayin wani abu da ke cikin ajandarta a yanzu.
A cewarsa, Iran ta samu wasu dalilai a tattaunawar da ta gabata da Amurka, lamarin da ya sa gwamnatin ta yi watsi da batun komawa teburin sulhu a wannan lokaci.
