Saturday, March 21, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Nijeriya na shirin yin doka kan kananan yara masu amfani da...

Gwamnatin Nijeriya na shirin yin doka kan kananan yara masu amfani da shafukan sada zumunta

Gwamnatin Nijeriya ta fara neman ra’ayoyin jama’a kan yiwuwar yin doka da za su kare yara a intanet, ciki har da kayyade shekarun da yara za su iya amfani da kafafen sada zumunta.

Ministan sadarwa da kirkire-kirkire, Bosun Tijani, ne ya sanar da wannan shiri a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Talata.

Google search engine

Ya bayyana cewa duk da cewa intanet na ba yara damar koyo, kirkira da sadarwa, amma yana iya jefa su cikin hadurruka kamar cin zarafi a yanar gizo, kallon abubuwan da ba su dace ba, da kuma barazanar da sabbin fasahohi ke haifarwa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata