Saturday, March 21, 2026
HomeLabaraiKotu ta ɗage ci gaba da sauraron shari'ar tsohon ministan shari'a Abubakar...

Kotu ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar tsohon ministan shari’a Abubakar Malami da ɗansa

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron shari’ar tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami, tare da dansa Abdulaziz Malami, kan zargin daukar nauyin ta’addanci da kuma mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Kotun wadda Justice Joyce Abdulmalik ke jagoranta ta dage shari’ar zuwa ranakun 15 da 16 ga Afrilu, 2026, domin fara sauraron karar.

Google search engine

A zaman kotun da aka yi ranar Talata, lauyan masu gabatar da kara, Akinlolu Kehinde, ya sanar da kotu cewa an ba shi aikin jagorantar shari’ar ne kwanan nan, don haka yana bukatar karin lokaci domin ganawa da shaidu da kuma shirya takardun shari’ar.

Ya ce an ba shi umarnin karɓar shari’ar ne a ranar Litinin, don haka ya bukaci kotu ta ba su sabon lokaci domin su shirya yadda ya kamata.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata