Babbar kotun ma’aikata, reshen Kano, ta ci gwamnatin jihar Kano tarar Naira miliyan 1, a shari’ar da wasu tsofaffin kwamishinonin jihar suka shigar domin hana gwamnati karɓar motoci na aiki da aka ba su lokacin da suke kan mukamansu.
Kotun, wadda Justice Mahmood Abba Namtari ke jagoranta, ta yanke hukuncin ne a zaman da aka gudanar ranar Talata, inda ta ce gwamnati za ta bayar da dubu 200,000 a matsayin tara a kowanne daga cikin shari’o’i biyar da ke da alaka da batun.
A zaman kotun, lauyan gwamnatin Kano, S. U. Jibril, ya bayyana cewa bangaren gwamnati ba su shirya ci gaba da shari’ar ba, saboda an sanar da shi a kurarren lokaci, lamarin da ya ce bai ba shi isasshen lokaci ba wajen shirya takardun da ake bukata.
Sai dai Solace base ta rawaito cewa lauyan tsofaffin kwamishinonin, Suraj Sa’ed, ya ce ba su da matsala da bukatar dage shari’ar, amma ya roki kotu ta sanya tara domin diyya ga wadanda suka shigar da karar.
Bayan dogon nazari, kotu ta amince da dage sauraron karar tare da sanya tara ta N200,000 a kowace shari’a, sannan ta dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 28 ga Afrilu, 2026.
