Saturday, March 21, 2026
HomeLabaraiRuwan tafki ya ci ran wasu matasa biyu da suka yi gudun...

Ruwan tafki ya ci ran wasu matasa biyu da suka yi gudun tsira daga masu kwacen waya a Kano

Wasu matasa biyu sun rasa rayukansu bayan sun nutse a cikin wani tafki yayin da suke gudun wasu da ake zargin ‘yan kwacen waya ne a jihar Kano.

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da cewa lamarin ya faru ne a yankin Ring Road Kureken Sani da ke karamar hukumar Kumbotso.

Google search engine

Mai magana da yawun hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce matasan da suka rasu sun hada da Sadiq Isyaku mai shekaru 18 da kuma Auwal Isyaku.

Ya bayyana cewa jami’an kashe gobara sun ciro su daga cikin ruwan, amma daga bisani aka tabbatar da mutuwarsu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata