Saturday, March 21, 2026
HomeLabaraiKoriya ta Arewa ta zargi Amurka da Israel da haddasa rashin zaman...

Koriya ta Arewa ta zargi Amurka da Israel da haddasa rashin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya

Gwamnatin Koriya ta Arewa ta bayyana cewa tana girmama zabin da al’ummar Iran suka yi na naɗa sabon jagoran addini na kasar, yayin da ta zargi Amurka da Israel da haddasa rashin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa kafar yada labaran gwamnatin Koriya ta Arewa, ta bayyana cewa Pyongyang na mutunta ‘yancin al’ummar Iran na zabar sabon jagoransu.

Google search engine

A ranar Lahadi ne dai Iran ta sanar da nadin Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran addinin kasar, bayan rasuwar mahaifinsa Ali Khamenei, wanda ya mutu sakamakon wani hari da Israel ta kai a ranar 28 ga Fabrairu.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Koriya ta Arewa ya bayyana cewa kasarsa na girmama zabin da al’ummar Iran suka yi, yana mai zargin Amurka da Israel da lalata zaman lafiya da tsaro a yankin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata