Fargaba ta mamaye wasu kauyuka a jihar Katsina bayan wani mummunan rikici tsakanin kungiyoyin ‘yan bindiga da ya tilasta wa mazauna sama da kauyuka goma dakatar da sallar Juma’a saboda tsananin harbe-harben bindiga da ya dauki tsawon sa’o’i.
Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa rikicin ya faru ne a yankunan karkara da ke iyaka da kananan hukumomin Musawa, Kankara da kuma Malumfashi, inda aka yi musayar wuta tsakanin kungiyoyin ‘yan bindiga na tsawon lokaci, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin tsananin fargaba.
Rahotanni sun ce tun kafin lokacin sallar Juma’a, wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai farmaki a garin Dangani da rana tsaka, inda suka shiga garin kan babura fiye da 70.
Maharan sun lalata shagunan sayar da wayoyi tare da kwace wayoyin da ake cajawa a wuraren caji da kuma wadanda suka samu a hannun mazauna yankin.
