Aƙalla mutane uku ne ake fargabar sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon wani hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Jikamshi da ke ƙaramar hukumar Musawa a jihar Katsina.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:10 na yammacin ranar Talata, lokacin da wasu mazauna garin ke shirin buɗe baki a rana ta 21 ga watan Ramadan, inda ‘yan bindigar suka riƙa harbi ba kakkautawa tare da jefa al’umma cikin firgici.
Rahotanni sun ce maharan sun kuma shiga shaguna daban-daban a garin, inda suka wawushe kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.
Mutanen da suka jikkata a harin an garzaya da su asibiti domin samun kulawar likitoci.
