Saturday, March 21, 2026
HomeLabarai'Yan bindiga sun sake yin barna a jihar Katsina

‘Yan bindiga sun sake yin barna a jihar Katsina

Aƙalla mutane uku ne ake fargabar sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon wani hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Jikamshi da ke ƙaramar hukumar Musawa a jihar Katsina.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:10 na yammacin ranar Talata, lokacin da wasu mazauna garin ke shirin buɗe baki a rana ta 21 ga watan Ramadan, inda ‘yan bindigar suka riƙa harbi ba kakkautawa tare da jefa al’umma cikin firgici.

Google search engine

Rahotanni sun ce maharan sun kuma shiga shaguna daban-daban a garin, inda suka wawushe kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Mutanen da suka jikkata a harin an garzaya da su asibiti domin samun kulawar likitoci.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata