Saturday, March 21, 2026
HomeLabaraiDakarun sojin Nijar sun yi wani gagarumin aiki

Dakarun sojin Nijar sun yi wani gagarumin aiki

Rundunar sojin Nijar ta ce ta halaka akalla ‘yan ta’adda 265 tare da kama wasu 132 da ake zargi da taimaka musu ko aikata laifuka a sassa daban-daban na kasar cikin watan Fabrairu.

A wani rahoto da cibiyar kula da ayyukan hadin gwiwa ta soji ta fitar, ta ce sojojin sun gudanar da hare-haren hadin gwiwa na sama da kasa tare da sumame da kuma a tabbatar da tsaro a wurare daban-daban da ake gudanar da ayyukan soja.

Google search engine

A cewar rahoton, wadannan hare-hare sun kuma kai ga lalata da kwace motoci 47, bindigu 79, babura 152 da ake amfani da su wajen aikata laifuka.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata