Rundunar sojin Nijar ta ce ta halaka akalla ‘yan ta’adda 265 tare da kama wasu 132 da ake zargi da taimaka musu ko aikata laifuka a sassa daban-daban na kasar cikin watan Fabrairu.
A wani rahoto da cibiyar kula da ayyukan hadin gwiwa ta soji ta fitar, ta ce sojojin sun gudanar da hare-haren hadin gwiwa na sama da kasa tare da sumame da kuma a tabbatar da tsaro a wurare daban-daban da ake gudanar da ayyukan soja.
A cewar rahoton, wadannan hare-hare sun kuma kai ga lalata da kwace motoci 47, bindigu 79, babura 152 da ake amfani da su wajen aikata laifuka.
