DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NNPP ta kori jagora Kwankwaso

-

 

Google search engine

Jam’iyyar NNPP ta sanar da korar jagoranta Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso bayan da ta dakatar da shi makonni uku da suka gabata, sakamakon zargin sa da yiwa jam’iyyar zagon kasa tun bayan kammala babban zaben kasar.

Gidan rediyon Faransa, RFI Hausa, ya ce korar  ta Kwankwason na cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar dauke da sa hannun sakataren yada labaranta na kasa Abdulsalam Abdulrasaq.

Wannan dai na zuwa ne kasa da kwanaki uku bayan da wani tsagi na jam’iyyar ya sha alwashin gurfanar da tsohon gwamnan Kanon da wasu mabiyan sa a gaban shari’a, sakamakon zargin wadaka da fiye da naira biliyan 1 da aka tara a asusun jam’iyyar na kudaden sayar da fam din ‘yan Takara.

Sanarwar ta Abdulrasaq ta kuma kara da cewa korar kwanwason zata fara aiki ne nan take, yayin da yayi karin hasken cewa an dauki matakin ne bayan da Kwankwason ya ki bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar, sakamakon gayyatar sa da aka yi don amsa wasu tambayoyi. 

Sakataren yada labaran jam’iyyar ya kuma tabbatar da cewa korar Rabi’u Kwankwaso na da goyon baya a cikin kundin jam’iyyar na shekarar 2022.

To sai dai da yake jam’iyyar ta rabu gida biyu kan matakin korar ta Kwankwaso, guda daga cikin masu goyon bayan sa kuma mai bincken kudi na jam’iyyar Ladipo Johnson yace bangaren da suka kori Kwankwason basu da alkibla kwata-kwata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara