Friday, March 20, 2026
HomeLabaraiDSS ta kama wasu mutane da ake zargi da karkatar da tallafin...

DSS ta kama wasu mutane da ake zargi da karkatar da tallafin da gwamnatin tarayya ta bayar don rabawa jama’a

Hukumar tsaron sirri ta DSS a Najeriya ta sanar da kama wasu mutane
da hannu a karkatar da kayayyakin abincin da gwamnatin tarayya ta samar don
rabawa jama’a.

Google search engine

Hukumar ta ce duka mutanen da ta kama jami’an hukumar bayar da
agajin gaggawa na kasa NEMA ne, kuma mafi yawan su an kama su ne a kasuwar
Lafia da ke jihar Nasarawa lokacin da suke tsaka da sayar da kayan ga ‘yan
kasuwa.

Mai Magana da yawun hukumar Peter Afunanya
ya ce tuni aka kamo wasu kayayyakin da mutanen suke yunkurin sayarwa.

Afunanya ya kuma bukaci jama’ar Najeriya da su
sanya idanu sossai kan masu sayar da kayan abinci don basu rahoton masu sayar
da kayan da gwamnati ta tanadar don rabawa jama’a a kyauta.

Haka kuma hukumar ta ce ta kama wasu mutanen na
daban wadanda sune suke shirya yadda za’a sace kayan kafin ma a kai su kasuwa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata