DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Dikko ta raba N20m ga iyalan ‘yan sintirin da ‘yan ta’adda suka hallaka a Katsina

-

Gwamnatin jihar Katsina ta sanar da rarraba kudi Naira milyan 20 ga wasu daga cikin iyalai da ‘yan’uwan ‘yan sintirin Vigilante da ‘yan ta’adda suka hallaka a lokacin da suke bakin daga a jihar.
Sakataren Gwamnatin jihar Abdullahi Garba Faskari a lokacin rarraba kudin a Katsina, ya ce kudin wani tallafi ne ga iyalan mamatan ba wai diyyar rayukansu ba.
A nasa bangaren, babban mataimaki na musamman ga Gwamnan jihar Katsina kan ‘yan gudun hijra da wadanda iftila’i ya fada mawa Sa’id Ibrahim Danja ya ce gwamnatin ta kuma dauki nauyin kula da lafiyar duk jami’an da aka raunata a lokacin da suke kokarin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar yankunansu.
Ya ce akwai jami’an tsaro 4 da mutanen gari 32 da ke kwance a asibitin kashi na ‘Orthorpaedic Katsina’ da asibitin koyarwa na Federal Teaching Hospital, Katsina inda suke karbar magani da kulawar likitoci duk kyauta bayan da gwamnatin Dikko ta dauke musu dawainiyar.
Ya ce wannan tallafi an yi shi ne da zummar tallafar wadanda suka samu raunuka da iyalan wadanda suka rasu a lokacin arangama da ‘yan ta’adda musamman a kananan hukumomin da ke fama da karancin tsaro a jihar.
Hon Sa’id Ibrahim Danja ya ce iyalan ‘yan sintiri 33 ne suka amfana da wannan tallafin kudin, inda aka rarraba musu Naira dubu dari biyar-biyar, a yayin da wadanda suka samu raunuka su 10 suka samu Naira dubu 250 kowane.
Kazalika, akwai wani jami’in dan sanda mai mukamin ‘Insfekta’ da ya samu rauni aka bashi gudunmuwa kudi Naira dubu 250 sai jinjirin matar wani soja da ya rasa ransa a filin daga aka bata gudunmuwr kudi Naira milyan 1. Bayanai dai sun ce ‘yan ta’addar sun hallaka wannan soja ne a ranar da ake sunan jaririn.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara