DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar likitoci ta ba gwamnatin Abba Gida-Gida sa’o’i 48 kan zargin cin zarafin likita

-

Kungiyar likitocin Nijeriya reshen jihar Kano, ta ba da wa’adi ga gwamnatin jihar da ta gaggauta korar kwamishiniyar jin kai, Amina Abdullahi, sakamakon cin zarafin wata likita.

Google search engine

A wata sanarwa da shugaban Kungiyar, Dr. Abdurrahman Ali da Sakatare, Dr. Ibrahim D. Muhammad suka sanya wa hannu, kungiyar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 1 ga watan Nuwamba a sashin kula da kananan yara na asibitin kwararru na Murtala Muhammad.

A cewar sanarwar, an yi zargin Kwamishinar da mukarrabanta da jami’an tsaro suka ci zarafin likitar. 

Zargin cin zarafin dai ya samo asali ne sakamakon rashin samun magungunan da aka rubuta wa marasa lafiya, yayin da ta ke kula da marasa lafiya sama da 100.

Biyo bayan wannan al’amari, kungiyar Kano ta yi barazanar dakatar da aikin jinya a asibitin kwararru na Murtala Muhammad cikin sa’o’i 48, idan ba a biya musu bukatunsu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara