DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar likitoci ta ba gwamnatin Abba Gida-Gida sa’o’i 48 kan zargin cin zarafin likita

-

Kungiyar likitocin Nijeriya reshen jihar Kano, ta ba da wa’adi ga gwamnatin jihar da ta gaggauta korar kwamishiniyar jin kai, Amina Abdullahi, sakamakon cin zarafin wata likita.

Google search engine

A wata sanarwa da shugaban Kungiyar, Dr. Abdurrahman Ali da Sakatare, Dr. Ibrahim D. Muhammad suka sanya wa hannu, kungiyar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 1 ga watan Nuwamba a sashin kula da kananan yara na asibitin kwararru na Murtala Muhammad.

A cewar sanarwar, an yi zargin Kwamishinar da mukarrabanta da jami’an tsaro suka ci zarafin likitar. 

Zargin cin zarafin dai ya samo asali ne sakamakon rashin samun magungunan da aka rubuta wa marasa lafiya, yayin da ta ke kula da marasa lafiya sama da 100.

Biyo bayan wannan al’amari, kungiyar Kano ta yi barazanar dakatar da aikin jinya a asibitin kwararru na Murtala Muhammad cikin sa’o’i 48, idan ba a biya musu bukatunsu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijeriya za ta kara mayar da hankali kan tsaurara matakan kudi da gyaran haraji a 2026 – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa shekarar 2026 ta zo da sabon mataki mai karfi na bunkasar tattalin arziki, inda ya ce gyare-gyaren...

Bankunan Nijeriya za su fara cire harajin N50 daga masu tura kudi ta banki da suka kai N10,000

Daga 1 ga watan Janairun, 2026, bankunan Nijeriya za su fara cire harajin N50 kan duk wanda ya tura kudi da ya kai ₦10,000 ko...

Mafi Shahara